Hukumar Yan Sanda ta Jahar Legas ta Kama Wasu Ma’aurata biyu Abisa Zargin Cin Zarafin Yayansu ta Hanyar Duka.
Ƴan sanda sun kama wasu iyaye a Legas bisa zargin cin zarafin ƴaƴansu biyu.
Jami’an ƴan Sandar Nijeriya reshen Jihar Legas Sun kama wannan mata Busola Oyediran da Mijinta Akebiara Emmanuel da ke Egbeda Legas a jiya Juma’a 13 ga watan Janairu 2022 biyo bayan ƙorafe-ƙorafe da makwabta suka yi kan cin zarafin ƴaƴansu masu shekaru 5 da 2 a kai a kai.