Rayuwa Kenan! Duniya Ba Wajen Zama Ba

 Wani mutum mai shekaru 36 da haihuwa da aka bayyana sunansa da Owolabi Musiliu ya shiga komar ‘yan sandan jihar Ogun bisa zarginsa da kashe budurwarsa, Fausat Idowu.

Musiliu, wanda bakanike ne ya dauki budurwarsa Fausat mai shekaru 40 da haihuwa zuwa otal a Abeokuta don su biya bukatar juna, kawai sai Fausat wacce bazawara ce mai ‘ya’ya 4 ta kama rashin lafiya kuma kan kace me, ta sheka barzahu.

A jawabi Musiliu da ya gabatar ga manema labarai a lokacin da kwamishina ‘yan sandan jihar Ogun, Ahmed Iliyasu ya yi holinsa a jiya Juma’a ya bayyana cewa wannan shi ne karo na farko da shi da budurwasa mai rasuwa suka nemi da su biya bukatar junansu tun bayan da suka fara soyayya wata shida da suka wuce.